Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya yi kira ga masu kamfani a babban birnin kasar nan da su ba da hadin kai ga hukumar babban birnin tarayya Abuja ta fuskar biyan haraji.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da wata tawaga daga kungiyar Nadeem, karkashin jagorancin mashawarci na musamman ga babban jamiāin gudanarwa, Mista George Tolofari, suka kai ziyarar ban girma ga hukumar gudanarwar babban birnin tarayya Abuja a ranar Larabar da ta gabata.
Wike ya bukaci kamfanoni a babban birnin tarayya Abuja da su tabbatar da biyan haraji cikin gaggawa, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta iya gina tituna da gine-ginen jamaāa ba tare da biyan haraji ba.
“Ina kuma ba ku kwarin gwiwar tabbatar da cewa kun biya haraji saboda abin da ke jan hankalin gwamnati,” in ji Wike.
āAbuja ba kamar sauran jihohin da suke samun kudi daga asusun tarayya ba. Muna dogara ne akan haraji kawaiā
Ya kuma ba da tabbacin cewa babban birnin tarayya Abuja na da aminci ga masu zuba jari su zo su zuba jari, ya kara da cewa tsaro da samar da ayyukan yi na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatin babban birnin tarayya ta sa a gaba, kamar yadda ajandar sabunta fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi.