A karo na biyu, kamfanin Air Peace ya sake mayar da martani ga masarautar Kano, bisa abinda ya faru makon ya gabata.
Masarautar Kano ce, ta bukaci kamfanin ya baiwa mai martaba Sarki hakuri bisa kin jinkirta tashin jirgin.
Air Peace ya baiwa daukacin kwastamominsa hakuri bisa abinda ya faru.
Shugabannin kamfanin Air Peace sun yi martani ga masarautar Kano cewa, su suka jinkirta jirginsa na Banjul daga kasar Gambia zuwa Legas makon da ya gabata.
A jawabin da kamfanin ya fitar a shafinsa na internet ranar Lahadi, ya bayyana cewa, jirgin Banjul zuwa Legas mai zaman kansa ne, ba shi da alaka da jirgin Legas da Kano.
“Jirgin iyakar tafiyarsa Legas kuma bai da alaka da wani waje, saboda haka, kamfanin ba zai san manufar fasinjojinsa ba. Amma muna baiwa abokan huldar mu hakuri da suka gaza isa, idan suka nufa kamar yadda suka so”.
Har yanzu dai Air Peace bai yi magana kan hakurin da masarautar Kano ta bukata ba. A cewar Legit.