fidelitybank

Har yanzu zafin kayi na damun ka Atiku – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya mayar wa babban mai hamayya da shi na Jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar da martani bayan sukar gwamnatinsa.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, kuma dan takarar shugaban kasa na babbar jami’iyyar hamayya ta PDP a zaben da ya gabata, ya bukaci shugaba Bola Tinubu ya sauka daga shugabancin kasar idan ba zai iya shawo kan matsalolin tsaron da kasar ke fama da su ba.

Atiku Abubakar, wanda shugaba Tinubu ya kayar a zaben da ya gabata, ya zargi shugaban da yin wasa da aikinsa yayin da kasar ke nutsewa cikin matsalar tsaro da ta tabarbarewar tattalin arziki.

Sai dai fadar shugaban Najeriyar ta yi watsi da kalaman na Atiku tana mai cewa wata suka ce irin ta ‘yan hamayya.

A sanarwar martani da ta fitar, fadar shugaba Bola Tinubu ta ce har yanzu zafin shan kaye ne ke damun Atiku.

“Mun san cewa har yanzu zafin shan kaye bai saki Atiku ba don haka zai iya furta komi na sukar shugaba Tinubu,” in ji sanarwar.

Mai magana da yawun shugaba Tinubu, malam Abdul’aziz Abdul’aziz a hirarsa da BBC ya ce tsohon mataimakin shugaban na son ya ci gaba da jan hankali ne.

“Wannan batu ne na ɗan adawa da yake son ya ja hankali domin a yi masa tafi domin mutum ne da ya faɗi zaɓe, saboda haka ƙoƙari yake a san da shi a riƙa jin sa a labarai domin kada a manta da shi,” in ji Abdul’aziz Abdul’aziz.

Ya ce duk wanda yake Najeriya ya san akwai shugaba mai cikakken iko kuma ko mutum ba ya ra’ayin gwamnatin APC ana ganin shugaban ƙasa da ganin aikinsa.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...
X whatsapp