Shugaban riko na kwamitin riko da tsare-tsare na babban taro na jam’iyyar APC, Abubakar Sani Bello, ya musanta karbar wata takardar mika mulki daga shugaban kwamitin Gwamna Mai Mala Buni.
Sani Bello, wanda ya mayar da martani kan wasikar da aka ce Buni ya rubuta na mika masa mukamin shugaban jam’iyyar na kasa, ya shaida wa manema labarai bayan taron kwamitin riko ya ce bai ga wasikar ba.
Wasikar ta Buni mai kwanan wata 28 ga Fabrairu, 2022, tana yawo a kafafen sada zumunta mai taken “Transmission of the National Chairman, CECPC”.
An ce: “Wannan don sanar da ku ne cewa zan fara ziyarar jinya zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) daga yau 28 ga Fabrairu 2022. Zan dawo ofis bayan an sallame ni daga asibiti. In ba ni, ina mika muku ayyukan ofishina a matsayina na Shugaban Kwamitin Tsare-tsare na Musamman na Kasa (CECPC) zuwa gare ku. A cewar wasikar Buni a cewar The Nation.