fidelitybank

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Date:

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da ɗaukar ɗumi, wasu manyan ƴan siyasa a babbar jam’iyyar adawa ta PDP sun nanata cewa har yanzu jam’iyyar tana nan da ƙarfinta kuma a dunƙule.

Shugabannin jam’iyyar sun kuma ce ana ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar don zaɓen shugabannin da za su ja ragamar ta.

Honarabul Isa Ashiru Kudan, wanda ya yi wa jam’iyyar PDP takarar gwamnan jihar Kaduna har sau biyu – a shekarar 2019 da kuma 2023, ya shaida wa BBC cewa suna ɗaukar matakai waɗanda yanzu har sun kai ga warware rikice-rikicen da suka dabaibaye jam’iyyar.

“A baya an yi ta samun hatsaniya tsakanin ƴan jam’iyyar mu, amma zuwa yanzu mun samu nasarar warware waɗannan rikice-rikice. Ba mu da wata matsala a yanzu.

“Mu ƴan jam’iyyar PDP ne ba mu cikin wata haɗaka. Ba laifi bane idan ƴan haɗakar suka zo don mu haɗa kai wajen kayar da gwamnatin da ke mulki da ceton al’ummar Nijeriya kan halin da suka tsinci kansu,” in ji Ashiru Kudan.

Ɗan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP a jihar Kaduna a zaɓen 2023 ya ce har yanzu jam’iyyarsu tana nan da karfinta, babu abin da ya sauya.

“PDP na nan kuma duk wanda ya zo za mu karɓe shi mu kuma rungume shi don tafiya tare. Da yardar Allah za mu dawo da kafafuwan mu,” in ji Ashiru.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp