fidelitybank

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Date:

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da ɗaukar ɗumi, wasu manyan ƴan siyasa a babbar jam’iyyar adawa ta PDP sun nanata cewa har yanzu jam’iyyar tana nan da ƙarfinta kuma a dunƙule.

Shugabannin jam’iyyar sun kuma ce ana ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar don zaɓen shugabannin da za su ja ragamar ta.

Honarabul Isa Ashiru Kudan, wanda ya yi wa jam’iyyar PDP takarar gwamnan jihar Kaduna har sau biyu – a shekarar 2019 da kuma 2023, ya shaida wa BBC cewa suna ɗaukar matakai waɗanda yanzu har sun kai ga warware rikice-rikicen da suka dabaibaye jam’iyyar.

“A baya an yi ta samun hatsaniya tsakanin ƴan jam’iyyar mu, amma zuwa yanzu mun samu nasarar warware waɗannan rikice-rikice. Ba mu da wata matsala a yanzu.

“Mu ƴan jam’iyyar PDP ne ba mu cikin wata haɗaka. Ba laifi bane idan ƴan haɗakar suka zo don mu haɗa kai wajen kayar da gwamnatin da ke mulki da ceton al’ummar Nijeriya kan halin da suka tsinci kansu,” in ji Ashiru Kudan.

Ɗan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP a jihar Kaduna a zaɓen 2023 ya ce har yanzu jam’iyyarsu tana nan da karfinta, babu abin da ya sauya.

“PDP na nan kuma duk wanda ya zo za mu karɓe shi mu kuma rungume shi don tafiya tare. Da yardar Allah za mu dawo da kafafuwan mu,” in ji Ashiru.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp