Fitaccen mawakin nan, Eedris Abdulkareem, ya ce shekaru 21 bayan ya fitar da wakarsa mai cike da cece-kuce mai suna ‘Jaga Jaga’ wadda ta tada zaune tsaye a Najeriya, har yanzu kasar na cikin rugujewa.
Ya koka da yadda al’amura ke kara ta’azzara, yana mai jaddada cewa canjin Dala zai kai N2,000.
Ya koka da halin kuncin da kasar ke ciki yayin da yake nuna bako a wani shiri na kwanan nan na The Honest Bunch Podcast wanda jarumi Chinedu Ani Emmanuel, aka Nedu, Deity Cole, da Miji Material suka shirya.
Abdulkareem ya ce, “Najeriya har yanzu Jaga Jaga shekaru 21 baya. Yunwa a ko’ina, mutane suna mutuwa. Yaya mutane za su tsira idan Dala ta kasance N1600? Goodluck Jonathan ya bar shi N198. [Muhammadu] Buhari ya kai Naira 300, [Bola] Tinubu ya kai N1600.
“Dollar na zuwa N2000. To ta yaya kuke son talakawa su rayu a kasar nan? Hatta Yarabawa da suke ta ihun ‘Emilokan’, su ne suke mutuwa da yunwa a yanzu.”