Gabanin zaben watan Fabrairun 2023, jam’iyyar Labour (LP) ta ce, ta na tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) Rabi’u Kwankwaso da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar domin yin kawance.
Babban Darakta Janar na Majalisar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa na Jamâiyyar Labour (LP) Doyin Okupe ne ya bayyana haka a ranar Jumaâa, a lokacin da ya yi jawabi a shirin gidan talabijin na Channels TV.
Dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar LP da Kwankwaso tun a farkon shekarar ne suka yi kawance, amma bangarorin biyu sun kasa cimma matsaya mai inganci.
Sai dai Okupe ya ce, har yanzu jamâiyyar ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen kulla kawance da Kwankwaso da tawagarsa da ke kada kuriâa a jihar Kano.
Ya ce, âA matsayinmu na jamâiyya, a matakin yakin neman zabenmu, muna magana da SDP; muna magana da Kwankwaso da tawagarsa kuma. Muna magana da PRP da ADC.
“Na yi imani kuma na yi imanin cewa Allah zai taimake mu daga yanzu zuwa Disamba, za mu hada kai da juna a siyasance a kasar nan da kuma kasa.”