fidelitybank

Har yanzu muhimman wurare ya na ƙarƙashin ikon mu – Shugaban Ukraine

Date:

shugaban ƙasar Ukraine, Zelensky, ya ce, har yanzu Ukraine na rike da muhimman wurare a mamayar da Rasha ta yi musu.

Har yanzu Ukraine na rike da muhimman yankunan kasar da sojojin Rasha ke kokarin kwacewa, in ji shugaban kasar Volodymyr Zelensky, makonni da dama da Rasha ke ci gaba da kai farmaki.

Sojojin Ukraine sun mayar da martani ga duk wani hari da sassan Rasha suka kai, in ji Zelensky a cikin wani sakon bidiyo da aka buga ta Telegram a ranar Juma’a.

Zelensky ya ce, mazauna garuruwa kamar Mariupol a Kudu, Kharkiv a Gabas da Chernihiv a Arewa, wadanda sojojin Rasha suka yi wa kawanya, ba za a bar su cikin kunci ba.

“Daga sojoji zuwa coci, kowa yana yin duk abin da zai iya ga mutanen Yukren.

“Za ku sami ‘yanci,” in ji shugaban.

Ya kuma gode wa shugaban Amurka, Joe Biden, saboda sabon taimakon da ya yi.

Zelensky ya yi alƙawarin ba wa ‘yan kasuwa taimako kamar ƙarancin ja da lamuni marasa riba a lokacin rikicin makami.

A halin da ake ciki, akwai alamun cewa gidan wasan kwaikwayo da aka kai wa hari a birnin Mariupol na Ukraine da aka yi wa kawanya, mai yiwuwa ya ƙunshi mutane fiye da yadda ake zato.

Dan majalisar dokokin Ukraine Serhiy Taruta, ya ce, akalla mutane 1,300 na iya fakewa a ginin lokacin da aka kai masa harin bam a ranar Laraba.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp