shugaban ƙasar Ukraine, Zelensky, ya ce, har yanzu Ukraine na rike da muhimman wurare a mamayar da Rasha ta yi musu.
Har yanzu Ukraine na rike da muhimman yankunan kasar da sojojin Rasha ke kokarin kwacewa, in ji shugaban kasar Volodymyr Zelensky, makonni da dama da Rasha ke ci gaba da kai farmaki.
Sojojin Ukraine sun mayar da martani ga duk wani hari da sassan Rasha suka kai, in ji Zelensky a cikin wani sakon bidiyo da aka buga ta Telegram a ranar Juma’a.
Zelensky ya ce, mazauna garuruwa kamar Mariupol a Kudu, Kharkiv a Gabas da Chernihiv a Arewa, wadanda sojojin Rasha suka yi wa kawanya, ba za a bar su cikin kunci ba.
“Daga sojoji zuwa coci, kowa yana yin duk abin da zai iya ga mutanen Yukren.
“Za ku sami ‘yanci,” in ji shugaban.
Ya kuma gode wa shugaban Amurka, Joe Biden, saboda sabon taimakon da ya yi.
Zelensky ya yi alƙawarin ba wa ‘yan kasuwa taimako kamar ƙarancin ja da lamuni marasa riba a lokacin rikicin makami.
A halin da ake ciki, akwai alamun cewa gidan wasan kwaikwayo da aka kai wa hari a birnin Mariupol na Ukraine da aka yi wa kawanya, mai yiwuwa ya ƙunshi mutane fiye da yadda ake zato.
Dan majalisar dokokin Ukraine Serhiy Taruta, ya ce, akalla mutane 1,300 na iya fakewa a ginin lokacin da aka kai masa harin bam a ranar Laraba.