fidelitybank

Har yanzu muhimman wurare ya na ƙarƙashin ikon mu – Shugaban Ukraine

Date:

shugaban ƙasar Ukraine, Zelensky, ya ce, har yanzu Ukraine na rike da muhimman wurare a mamayar da Rasha ta yi musu.

Har yanzu Ukraine na rike da muhimman yankunan kasar da sojojin Rasha ke kokarin kwacewa, in ji shugaban kasar Volodymyr Zelensky, makonni da dama da Rasha ke ci gaba da kai farmaki.

Sojojin Ukraine sun mayar da martani ga duk wani hari da sassan Rasha suka kai, in ji Zelensky a cikin wani sakon bidiyo da aka buga ta Telegram a ranar Juma’a.

Zelensky ya ce, mazauna garuruwa kamar Mariupol a Kudu, Kharkiv a Gabas da Chernihiv a Arewa, wadanda sojojin Rasha suka yi wa kawanya, ba za a bar su cikin kunci ba.

“Daga sojoji zuwa coci, kowa yana yin duk abin da zai iya ga mutanen Yukren.

“Za ku sami ‘yanci,” in ji shugaban.

Ya kuma gode wa shugaban Amurka, Joe Biden, saboda sabon taimakon da ya yi.

Zelensky ya yi alƙawarin ba wa ‘yan kasuwa taimako kamar ƙarancin ja da lamuni marasa riba a lokacin rikicin makami.

A halin da ake ciki, akwai alamun cewa gidan wasan kwaikwayo da aka kai wa hari a birnin Mariupol na Ukraine da aka yi wa kawanya, mai yiwuwa ya ƙunshi mutane fiye da yadda ake zato.

Dan majalisar dokokin Ukraine Serhiy Taruta, ya ce, akalla mutane 1,300 na iya fakewa a ginin lokacin da aka kai masa harin bam a ranar Laraba.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp