Jam’iyyar APC mai mulki ta jaddada cewa, shugaban kwamatin riƙo na jam’iyyar kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni zai karɓi aikinsa da zarar ya koma gida daga tafiyar da ya yi.
Lamarin na zuwa ne yayin da jam’iyyar ta fara shirin gudanar da babban taronta na ƙasa da za a yi ranar 26 ga watan Maris, inda za a zaɓi shugabanni a matakin ƙasa baki ɗaya duk da wani umarnin kotu da ya ce a dakatar da taron.
Sanawar da Sakataren Riƙo na Ƙasa John James Akpanudoedehe ya fitar ta sake jaddada cewa ba a sauke Mai Mala daga muƙamin ba, da kuma sauran ‘yan kwamatin kamar yadda wasu gwamnonin jam’iyyar suka bayyana a baya.
“Shirya sahihin taron ƙasa cikin nasara a ranar 26 ga watan Maris ne babban muradin kwamatin kuma za mu ci gaba da shirin yin hakan har zuwa lokacin da shugaba zai dawo kuma ya karɓi aikinsa,” a cewar sanarwar da sakataren kwamatin ya fitar ranar Talata.
Tuni aka fara sayar da fom ɗin takara ga masu son yin takarar shugabancin jam’iyyar kan naira miliyan 20.
Shugabancin APC ya shiga ruɗani ne a ƙarshen watan Fabarairu tun bayan da aka ga Gwamnan Neja Abubaukar Sani Bello ya fara jagorancin kwamatin. Daga baya kuma wata wasiƙa ta ɓulla cewa Mai Mala ne ya ba shi riƙo saboda ya yi tafiya ƙasar waje don a duba lafiyarsa.