fidelitybank

Har yanzu Mai Mala Buni ne shugaban riko na jam’iyyar – APC

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki ta jaddada cewa, shugaban kwamatin riƙo na jam’iyyar kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni zai karɓi aikinsa da zarar ya koma gida daga tafiyar da ya yi.

Lamarin na zuwa ne yayin da jam’iyyar ta fara shirin gudanar da babban taronta na ƙasa da za a yi ranar 26 ga watan Maris, inda za a zaɓi shugabanni a matakin ƙasa baki ɗaya duk da wani umarnin kotu da ya ce a dakatar da taron.

Sanawar da Sakataren Riƙo na Ƙasa John James Akpanudoedehe ya fitar ta sake jaddada cewa ba a sauke Mai Mala daga muƙamin ba, da kuma sauran ‘yan kwamatin kamar yadda wasu gwamnonin jam’iyyar suka bayyana a baya.

“Shirya sahihin taron ƙasa cikin nasara a ranar 26 ga watan Maris ne babban muradin kwamatin kuma za mu ci gaba da shirin yin hakan har zuwa lokacin da shugaba zai dawo kuma ya karɓi aikinsa,” a cewar sanarwar da sakataren kwamatin ya fitar ranar Talata.

Tuni aka fara sayar da fom ɗin takara ga masu son yin takarar shugabancin jam’iyyar kan naira miliyan 20.

Shugabancin APC ya shiga ruɗani ne a ƙarshen watan Fabarairu tun bayan da aka ga Gwamnan Neja Abubaukar Sani Bello ya fara jagorancin kwamatin. Daga baya kuma wata wasiƙa ta ɓulla cewa Mai Mala ne ya ba shi riƙo saboda ya yi tafiya ƙasar waje don a duba lafiyarsa.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp