fidelitybank

Har yanzu kadarori na da na mallaka tun a baya na ke juya wa – Buhari

Date:

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya ce kadarar da ya mallaka tun kafin ya hau mulki ba ta ƙaru ba har bayan saukarsa daga mulki a watan Mayun 2023.

Cikin wata sanarwa da kakakin tsohon shugaban, Mallam Garba Shehu ya fitar ya ce Buhari ya bayyana haka ne a lokacin ganawa da gwamnonin APC da suka kai masa ziyara a gidansa da ke Kaduna.

Tsohon shugaban ya shawarci gwamnonin na APC su rungumi aniyar hidimta wa al’umma, yana mai cewa shugabanci cike yake da tarin ƙalubale da kuma dama, kuma haɗa abubuwan biyu ne zai ciyar da ƙasa gaba.

Haka Muhammadu Buhari ya bayyana ƙwarin gwiwarsa kan gwamnonin na APC da irin nasarar da ya ce an samu samu a jihohinsu.

Tsohon shugaban ya kuma gode wa gwamnatin Tinubu saboda gyara masa gidansa na Kaduna.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya ce ƙungiyar tasu ta kai wa tsohon shugaban ziyarar barka da sallah, tare da bayyana godiyarsu da girmamawa ga tsohon shugaban kan gudunmowar da ya bayar ga dimokradiyya.

Tsohon shugaban ya gode wa gwamnonin kan ziyarar, yana mai cewa yayin da ya yi aiki da wasu wasun kuma sabbi ne a gare shi.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp