Dan wasan baya na Najeriya, William Troost-Ekong ya ce abu ne mai wahala a kawar da bakin cikin rashin samun nasarar lashe kofin gasar cin kofin Afrika na 2023.
Super Eagles ta kusa lashe kofin AFCON a karo na hudu amma ta sha kashi a hannun Cote d’Ivoire da ci 2-1 a wasan karshe.
Troost-Ekong ne ya baiwa Najeriya nasara a zagayen farko na wasan amma Cote d’Ivoire ta yunkuro domin samun nasara a wasan ta hannun Franck Kessie da Sebastien Haller.
Dan wasan bayan wanda ya ci wa Super Eagles kwallaye uku a gasar ya lashe kyautar dan wasan.
Da yake tsokaci kan ficewar Super Eagles a AFCON 2023, Troost-Ekong ya ce abu ne mai wahala a yi rashin nasara a wasan karshe a lokacin da suke kusa da daukaka.
“A Ć™arshe ya kasance mai É—aci-mai daÉ—i,” ya gaya wa CNN World Sports.
“Lokacin da kuka kusanci abin da kuke so ku yi shi ne lashe ta, kuma ina ganin yadda aka fitar da gasar tare da wasu kasashe masu sha’awar ganin kamar komai yana mana aiki.
“Yin rashin nasara a wasan karshe abu ne mai wahala, amma gaskiya Ivory Coast ta fi mu a ranar.
“Amma na kawo gida na dan wasan gasar wanda wani abu ne na musamman kuma abin da ba na tsammani kwata-kwata.
“Har yanzu da na canza shi don lambar yabo ta mai nasara ko da yake.”