fidelitybank

Har yanzu ban yanke shawara ko zan marawa Atiku baya ba a zaben 2023 ko a’a – Ortom

Date:

Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai, ya ce, har yanzu yana addu’ar Allah ya yi masa jagora kafin ya yanke shawarar ko zai goyi bayan Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023 ko kuma a’a.

Ortom wanda ya yi hira da Arise TV a ranar Laraba inda ya ce zai goyi bayan takarar shugaban kasa na Atiku ne kawai idan Allah ya kaimu, ya kuma bayyana rashin jin dadinsa kan yadda tsohon mataimakin shugaban kasar bai zabi Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas a matsayin mataimakinsa ba.

A watan Mayu ne Gwamna Wike ya zo na biyu bayan Atiku a lokacin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma bayan nasarar Atiku, jam’iyyar ta kafa kwamitin da zai zabi wanda zai tsaya takara.

An bayyana cewa a cikin mutane ukun da aka gabatar wa kwamitin, Wike ya samu kuri’u mafi yawa amma daga karshe Atiku ya zabi Gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta a matsayin abokin takararsa. Matakin na Atiku ya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin duk wadanda abin ya shafa da kuma magoya bayansu.

 

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp