Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kebbi, (KSUSTA) a ranar Larabar da ta gabata ta musanta cewa, ta dakatar da kungiyar malaman jami’o’in da ke ci gaba da yajin aikin na kasa.
Sakataren ilimi na Jami’ar, Abdulazeez Salihu, a cikin wata takardar sanarwa mai dauke da kwanan watan 24 ga watan Agusta, 2022, ya bayyana cewa za a ci gaba da harkokin ilimi a Jami’ar.
Amma, shugaban ASUU a jihar, Kwamared Yale Ibrahim ya ce babu wani ma’aikacin ilimi da zai koma kamar yadda sakataren ilimi na Jami’ar ya sanar har sai an janye yajin aikin a matakin kasa.
Ibrahim ya ce: “Muna so mu bayyana a nan cewa har yanzu Jami’ar tana yajin aiki kuma babu wani ma’aikacin ilimi da zai koma aiki a wannan ranar kamar yadda wasikar ta kunsa.
Ya umurci dukkan ma’aikatan ilimi da su bi ta hanyar zama a gida har sai kungiyar ASUU ta kasa ta dakatar da yajin aikin.
“ASUU, KSUSTA na ci gaba da tsayawa tsayin daka kan ci gaba da yajin aikin na kasa har sai an samu sanarwa,” in ji shi.