fidelitybank

Har yanzu ba mu karbi kudi daga Kungiyar Dillalan Man Fetur ba – Matatar Dangote

Date:

Matatar Ɗangote ta ce, har yanzu ba ta karɓi kuɗi daga ƙungiyar dillalan mai ta Najeriya Ipman ba domin sayen tataccen mai.

Wata sanarwa da matatar ta fitar a shafin X, ta ce ana tattaunawa da Ipman sai dai ta ce bai dace mambobin Ipman su nuna cewa suna fuskantar matsala ba wajen sayen tataccen mai daga matatarmu kasancewar “babu wata alaƙar kasuwanci ta kai tsaye da Ipman.

A cewar matatar ta Ɗangote, cikin sanarwar da jami’inta na hulɗa da jama’a, Anthony Chiejina ya sanyawa hannu, “an biya kuɗin da ake magana a kai ta hannun kamfanin mai na NNPCL, ba wurinmu ba.”

“NNPCL ba ta amince da kuɗin ba, kuma ba ta ba mu izinin bai wa Ipman mai ba.” in ji sanarwar.

Matatar ta ce “muna son mu jaddada cewa za mu iya wadatar da Najeriya da duk albarkatun mai har da man jirgi.”

“A yanzu, muna iya fitar da tirela 2,900 na mai duk rana kuma muna fitar da albarkatun mai ta hanyar ruwa.” in ji matatar Ɗangote.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp