fidelitybank

Har yanzu ba mu kara jin duriyar Manoma 21 da ‘yan Bindiga su ka sace ba – Mazauna Kebbi

Date:

Bayanai na cewa ana can cikin damuwa, dangane da batun wasu manoma 21 da ‘yan bindiga suka sace a garin Bena na yankin ƙaramar hukumar Danko-Wasagu na jihar Kebbi.

An sace manoman ne yayin da suke aiki a gonakinsu a farkon wannan mako.

Jama’ar yankin na Danko Wasagu ta gabas dai sun kwashe tsawon aƙalla shekara biyar suna fama da wannan matsala ta hare-haren ‘yan bindiga.

Tun da ‘yan bindigar suka sace manoman daga gonakinsu, a garin Bena na yankin karamar hukumar Danko/Wasagu ta jihar Kebbi, ake dakon jin duriyar inda aka yi da su. Amma har yanzu ba amo ba labari, a cewar wani mutumin yakin.

Ya shaida wa BBC cewa kwana kusan biyar da ɗauke mutanen amma har yanzu shiru.

Matsalar hare-haren da ‘yan bindigan ke kai wa yankin na Bena dai ta kai intaha kamar yadda wani mazaunin garin ya ce.

A cewarsa akwai ƙauyuka da dama da ɓarayin daji suka mamaye kuma sun hana mutane zama ko ma zuwa gona.

Dangane da matakan tsaro da ake ɗauka, game da wannan matsala ta ‘yan bindiga, sai mutumin na yankin Bena ya ce ana ɗaukan matakai amma ba su wadata ba.

Ya ce akwai buƙatar gwamnati ta kawo masu ɗauki domin cire su daga ƙangin da suka tsinci kansu ciki.

Mun dai yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar ta Kebbi, game da manoman ashirin da daya da ‘yan bindiga suka sace a yankin na Bena. Amma bai amsa kiraye-kirayen da muka yi masa, da saƙon da muka aika masa a rubuce ta waya ba.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp