fidelitybank

Har yanzu ba mu kara jin duriyar Manoma 21 da ‘yan Bindiga su ka sace ba – Mazauna Kebbi

Date:

Bayanai na cewa ana can cikin damuwa, dangane da batun wasu manoma 21 da ‘yan bindiga suka sace a garin Bena na yankin ƙaramar hukumar Danko-Wasagu na jihar Kebbi.

An sace manoman ne yayin da suke aiki a gonakinsu a farkon wannan mako.

Jama’ar yankin na Danko Wasagu ta gabas dai sun kwashe tsawon aƙalla shekara biyar suna fama da wannan matsala ta hare-haren ‘yan bindiga.

Tun da ‘yan bindigar suka sace manoman daga gonakinsu, a garin Bena na yankin karamar hukumar Danko/Wasagu ta jihar Kebbi, ake dakon jin duriyar inda aka yi da su. Amma har yanzu ba amo ba labari, a cewar wani mutumin yakin.

Ya shaida wa BBC cewa kwana kusan biyar da ɗauke mutanen amma har yanzu shiru.

Matsalar hare-haren da ‘yan bindigan ke kai wa yankin na Bena dai ta kai intaha kamar yadda wani mazaunin garin ya ce.

A cewarsa akwai ƙauyuka da dama da ɓarayin daji suka mamaye kuma sun hana mutane zama ko ma zuwa gona.

Dangane da matakan tsaro da ake ɗauka, game da wannan matsala ta ‘yan bindiga, sai mutumin na yankin Bena ya ce ana ɗaukan matakai amma ba su wadata ba.

Ya ce akwai buƙatar gwamnati ta kawo masu ɗauki domin cire su daga ƙangin da suka tsinci kansu ciki.

Mun dai yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar ta Kebbi, game da manoman ashirin da daya da ‘yan bindiga suka sace a yankin na Bena. Amma bai amsa kiraye-kirayen da muka yi masa, da saƙon da muka aika masa a rubuce ta waya ba.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp