Ana ci gaba da ƙidaya ƙuri’u a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa a Ghana bayan gudanar da zaɓen a cikin kwanciyar hankali.
Ana sa ran fara samun sakamakon wucin-gadi na zaɓen daga yau Lahadi.
‘Yan sanda sun ce mutum guda ya rasu sakamakon harbin bindiga a arewacin ƙasar lokacin wani rikicin zaɓe.
Matsawar babu ɗan takarar da ya samu fiye da kashi 50 cikin 100 na ƙuri’in da aka kaɗa to za a je zagaye na biyu a zaɓen.