fidelitybank

Har yanzu akwai kusan ƴan makarantar Chibok 20 a hannun ƴan ta’adda – Waɗanda suka tsira

Date:

Dakarun rundunar soji ta Operation Hadin Kai, sun ceto wasu ‘yan matan Chibok biyu a dajin Sambisa.

Wannan ya zo ne shekaru takwas bayan da mayakan Boko Haram suka sace dalibai mata 276 masu shekaru 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno a watan Afrilun 2014.

A makon jiya ne jaridar THEWILL ta bayar da rahoton cewa, an ceto ‘yan matan biyu, Mariam Dauda da Hauwa Joseph, tare da jariransu a yankin Gazuwa da ke karamar hukumar Bama, jihar Borno, a hannun sojojin da suka yi.

A yayin da suke bayyana irin wahalar da suka sha a dajin na tsawon shekaru 8 a wani taron manema labarai da suka gudanar a cibiyar kwamanda da kula da ‘yan gudun hijira da ke Maimalari Cantonment a Maiduguri a ranar Talata, sun bayyana cewa, sun daura aurensu da kwamandojin Boko Haram na tsawon shekaru kuma sun haifa musu jarirai.

Sun kuma bayyana cewa, sojojin Najeriya sun kashe mazajensu watanni da suka gabata.

Yayin da take amsa tambayoyin manema labarai, Maryam a yanzu Mariam ta ce, “Eh, har yanzu akwai sauran ‘yan matan Chibok a dajin Sambisa. Sun kuma yi aure, aƙalla sama da 20 suna nan.

Shaibu ya ce, an kubutar da Hauwa Joseph tare da danta ne a ranar 12 ga watan Yuni, 2022, a karamar hukumar Bama, yayin da Mary Dauda kuma aka kubutar da danta a ranar 14 ga watan Yuni, a lokacin da sojoji ke sintiri a yakin da suke a yankin.

Ya ce, duk ‘yan matan da ‘ya’yansu an yi musu duban lafiya da kuma kula da su, kafin a mika su ga gwamnati wadda daga baya za ta sada su da iyayensu.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp