fidelitybank

Har yanzu akwai ƴan matan Chibok 82 da ba su koma gida ba – Jeff

Date:

Yayin da ake cika shekara 11 da sace ƴan matan sakandaren Chibok da ƙungiyar Boko Haram ta yi a jihar Borno, har yanzu akwai ƴan mata 82 da ba su koma gida ba.

An sace ‘yan matan ne su 276 a ranar 14 ga watan Afrilun, 2014 – wannan mummunan al’amari na sace ƴan matan ya tayar da hankalin duniya a lokacin.

Mai magana da yawun ƙungiyar masu fafutukar ganin an saki sauran ƴan matan, Jeff Okoroafor, ya ce har yanzu iyayen waɗanda ƴaƴansu ba su koma gida ba na rayuwa cikin kunci.

Cikin abubuwan da ƙungiyar ke buƙata sun haɗa da; faɗa wa iyayen ƴan matan 82 da ƴaƴansu ba su koma gida ba ƙoƙari da ake yi na kuɓutar da su, da kuma fitar da rahoton Janar Ibrahim Sabo kan sace ƴan matan da kuma sanin irin matakin da gwamnati ta ɗauka ga waɗanda ke da hannu.

Sanarwar da ƙungiyar ta fitar, ta ce abin kunya ne ga gwamnatin Najeriya ko kuma gazawar jami’an tsaro na ƙasa ceto sauran ƴan matan, shekara 11 da sace su – inda ta ce hakan ya nuna cewa gwamnati ba ta damu da ƴan ƙasarta ba.

“Muna jin ciwo duk lokacin da muka tuna sace ƴaƴan mu. Muna buƙatar gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen ganin ta ceto sauran ƴan mata, samar da tallafi ga waɗanda suka tsira da kuma hukunta masu laifi,” in ji sanarwar ƙungiyar.

Gwamnatin Najeriya dai ta sha yin alkawarin ceto sauran ƴan matan na Chibok, sai dai har yanzu babu labarinsu.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp