fidelitybank

Har yanzu akwai ƴan matan Chibok 82 da ba su koma gida ba – Jeff

Date:

Yayin da ake cika shekara 11 da sace ƴan matan sakandaren Chibok da ƙungiyar Boko Haram ta yi a jihar Borno, har yanzu akwai ƴan mata 82 da ba su koma gida ba.

An sace ‘yan matan ne su 276 a ranar 14 ga watan Afrilun, 2014 – wannan mummunan al’amari na sace ƴan matan ya tayar da hankalin duniya a lokacin.

Mai magana da yawun ƙungiyar masu fafutukar ganin an saki sauran ƴan matan, Jeff Okoroafor, ya ce har yanzu iyayen waɗanda ƴaƴansu ba su koma gida ba na rayuwa cikin kunci.

Cikin abubuwan da ƙungiyar ke buƙata sun haɗa da; faɗa wa iyayen ƴan matan 82 da ƴaƴansu ba su koma gida ba ƙoƙari da ake yi na kuɓutar da su, da kuma fitar da rahoton Janar Ibrahim Sabo kan sace ƴan matan da kuma sanin irin matakin da gwamnati ta ɗauka ga waɗanda ke da hannu.

Sanarwar da ƙungiyar ta fitar, ta ce abin kunya ne ga gwamnatin Najeriya ko kuma gazawar jami’an tsaro na ƙasa ceto sauran ƴan matan, shekara 11 da sace su – inda ta ce hakan ya nuna cewa gwamnati ba ta damu da ƴan ƙasarta ba.

“Muna jin ciwo duk lokacin da muka tuna sace ƴaƴan mu. Muna buƙatar gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen ganin ta ceto sauran ƴan mata, samar da tallafi ga waɗanda suka tsira da kuma hukunta masu laifi,” in ji sanarwar ƙungiyar.

Gwamnatin Najeriya dai ta sha yin alkawarin ceto sauran ƴan matan na Chibok, sai dai har yanzu babu labarinsu.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp