Hukumomi sun ce har yanzu ba a ga fiye da mutum 100 ba, bayan kifewar wani kwale-kwale ɗauke da sama da mutum 200 a jihar Kogi.
Har yanzu masu ninƙaya da ƙwararrun shiga ruwa na ci gaba da aikin ceto domin lalubo mutane da gawarwakin waɗanda suka mutu.
Cikin wata sanarwa da ofishin gwamnan jihar Kogi ya fitar, ya tabbatar da ceto aƙalla mutum 24, waɗanda yanzu haka ke karɓar magani a asibitoci.
Jami’an bayar da agajin gaggawa sun ce kawo yazu an lalubo gawarwaki 27 a daidai inda lamarin ya faru.
Kwale-kwalen – wanda ke kan hanyarsa ta zuwa kasuwar Katcha da ke ci mako-mako a jihar Neja – ɗauke da fasinjoji waɗanda galibi ‘yan kasuwa ne da manoma ya nutse a yankin Dambo-Ebuchi na Kogin Neja
Kawo yanzu ba a san musabbabin hatsarin ba. Akwai alamun da ke nuna cewa da dama daga cikin fasinjojin ba sa sanye da rigunan kariya lokacin faruwar hatsarin.
Hatsarin shi ne irinsa na uku da aka samu a Najeriya cikin wata biyu. A watan da ya gabata wani ƙaton kwale-kwale ɗauke da fasinjoji kusa 300 ya kife a tsakiyar Kogin Neja inda kusan mutum 200 suka rasa rayukansu.
Ko a makon da ya gabata wasu mutum biyar sun mutu bayan da wasu jiragen ruwa biyu suka yi hatsari a jihar Delta da ke kudancin ƙasar.