fidelitybank

Har yanzu a na neman mutane 100 daga cikin wanda suka nutse a Neja

Date:

Hukumomi sun ce har yanzu ba a ga fiye da mutum 100 ba, bayan kifewar wani kwale-kwale ɗauke da sama da mutum 200 a jihar Kogi.

Har yanzu masu ninƙaya da ƙwararrun shiga ruwa na ci gaba da aikin ceto domin lalubo mutane da gawarwakin waɗanda suka mutu.

Cikin wata sanarwa da ofishin gwamnan jihar Kogi ya fitar, ya tabbatar da ceto aƙalla mutum 24, waɗanda yanzu haka ke karɓar magani a asibitoci.

Jami’an bayar da agajin gaggawa sun ce kawo yazu an lalubo gawarwaki 27 a daidai inda lamarin ya faru.

Kwale-kwalen – wanda ke kan hanyarsa ta zuwa kasuwar Katcha da ke ci mako-mako a jihar Neja – ɗauke da fasinjoji waɗanda galibi ‘yan kasuwa ne da manoma ya nutse a yankin Dambo-Ebuchi na Kogin Neja

Kawo yanzu ba a san musabbabin hatsarin ba. Akwai alamun da ke nuna cewa da dama daga cikin fasinjojin ba sa sanye da rigunan kariya lokacin faruwar hatsarin.

Hatsarin shi ne irinsa na uku da aka samu a Najeriya cikin wata biyu. A watan da ya gabata wani ƙaton kwale-kwale ɗauke da fasinjoji kusa 300 ya kife a tsakiyar Kogin Neja inda kusan mutum 200 suka rasa rayukansu.

Ko a makon da ya gabata wasu mutum biyar sun mutu bayan da wasu jiragen ruwa biyu suka yi hatsari a jihar Delta da ke kudancin ƙasar.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp