Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jin daɗi da godiyarsa ga ƴan Najeriya bisa addu’o’in da suka yi masa na cika shekara 73 a duniya.
Tinubu ya bayyana haka a taron buɗa- baki na musamman da ya jagoranta a fadar gwamnatin ƙasar a daren Asabar domin murnar zagayowar ranar haihuwarsa, kamar yadda mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya bayyana a wata sanarwa.
Da yake jawabi kan fafatukar da ya sha kan zaɓensa na shekarar 2023, Tinubu ya ce sai da ya kusa haƙura da takarar baki ɗaya saboda ƙalubale.
“Waɗanda suke kusa da ni sai suka fara tunanin ba zan kai ga gaci ba. Wani daga cikinsu ya taɓa samuna, ya ce min yana neman naira dubu 50 ne zai saya wa wani kawunmu abinci. Ya ce min saboda ni babu tsabar kuɗi a gari, mutane suna ta wahalar neman tsabar kuɗi. Kuma kawunmu ɗin attajiri ne, amma ko naira 10,000 babu a hannunsa.
“Da na miƙa masa tsabar kuɗin naira 50,000, sai ya kalle ni ya ce min da wahala in samu nasara, ni kuma na ce masa zan samu nasara.”
Tinubu ya ce a lokacin ne jikinsa ya yi sanyi har ya fara tunanin ajiye takarar, “amma sai Aminu Masari ya ƙarfafa min gwiwa, ya ce ba matsala, kada in juya baya,” in ji shi.
Tinubu ya ƙara da cewa ya karɓi ƙasar ne a daidai lokacin da take fama da matsin tattalin arziki, “shi ya sa na yanke shawarar ɗaukar matakai masu tsauri tun a farko a mulki, ciki har cire tallafin man fetur wanda ba ya cikin asalin jawabin da zan yi.”