fidelitybank

Har na cire raina da samun tikitin takara a 2023 – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jin daɗi da godiyarsa ga ƴan Najeriya bisa addu’o’in da suka yi masa na cika shekara 73 a duniya.

Tinubu ya bayyana haka a taron buɗa- baki na musamman da ya jagoranta a fadar gwamnatin ƙasar a daren Asabar domin murnar zagayowar ranar haihuwarsa, kamar yadda mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya bayyana a wata sanarwa.

Da yake jawabi kan fafatukar da ya sha kan zaɓensa na shekarar 2023, Tinubu ya ce sai da ya kusa haƙura da takarar baki ɗaya saboda ƙalubale.

“Waɗanda suke kusa da ni sai suka fara tunanin ba zan kai ga gaci ba. Wani daga cikinsu ya taɓa samuna, ya ce min yana neman naira dubu 50 ne zai saya wa wani kawunmu abinci. Ya ce min saboda ni babu tsabar kuɗi a gari, mutane suna ta wahalar neman tsabar kuɗi. Kuma kawunmu ɗin attajiri ne, amma ko naira 10,000 babu a hannunsa.

“Da na miƙa masa tsabar kuɗin naira 50,000, sai ya kalle ni ya ce min da wahala in samu nasara, ni kuma na ce masa zan samu nasara.”

Tinubu ya ce a lokacin ne jikinsa ya yi sanyi har ya fara tunanin ajiye takarar, “amma sai Aminu Masari ya ƙarfafa min gwiwa, ya ce ba matsala, kada in juya baya,” in ji shi.

Tinubu ya ƙara da cewa ya karɓi ƙasar ne a daidai lokacin da take fama da matsin tattalin arziki, “shi ya sa na yanke shawarar ɗaukar matakai masu tsauri tun a farko a mulki, ciki har cire tallafin man fetur wanda ba ya cikin asalin jawabin da zan yi.”

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp