Yayin da ake ci gaba da ƙidaya ƙuri’u a zaɓen shugaban Amurka, a yanzu hankali ya karkata kan jihohi marasa tabbas da za su iya tabatar da wanda ya yi nasara a zaɓen.
Kawo yanzu dai Donald Trump na jam’iyyar Republican ne ke kan gaba da ƙuri’un wakilan masu zaɓe 230, yayin da Kamala Harris ke da 165.
An dai bayyana sakamakon jihar North Carolina – wadda ke cikin jihohin bakwai – Inda kuma Donald Trump ya lashe ta.