fidelitybank

Hangen nesa ne ya sanya Tinubu zama shugaban ECOWAS

Date:

Tsohon dan majalisar wakilai, Shina Abiola Peller, ya bayyana cewa, sa shugaba Tinubu a matsayin shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) na tabbatar da hangen nesan wadanda suka kafa Najeriya.

Peller wanda ya wakilci mazabar Iseyin/Itesiwaju/Iwajowa/Kajola na tarayya tsakanin shekarar 2019 zuwa 2023 ya bayyana hakan a ranar Litinin.

Ku tuna cewa a ranar Lahadi ne aka ayyana shugaba Tinubu a matsayin shugaban kungiyar reshen yankin.

Peller ya bayyana cewa wadanda suka kafa Najeriya a kodayaushe suna son Najeriya ta zama Najeriya, ba wai Najeriya ce ta ‘yan Najeriya kadai ba.

A cikin wata sanarwa da aka rabawa DAILY POST a ranar Litinin, ya ce Tinubu a matsayinsa na shugaban kungiyar ECOWAS ya gabatar da sabon buri ga nahiyar Afirka.

Yayin da yake nanata cewa shekarar 2023 za ta zama wani sauyi ga Najeriya, Pellar ya ce, “Wannan wata shaida ce da hangen nesa na kakanninmu da suka kafa kasar da a kodayaushe suke son ganin an samar da Najeriya ga Afirka, tare da tabbatar da ci gaba da jagorancin tattalin arziki da siyasa a nahiyar Afirka.

“Shugaba Bola Tinubu a matsayin shugaban ECOWAS ya gabatar da sabon fatan alheri ga Nahiyar Afrika.

“Kamar yadda na sha fada a kodayaushe cewa 2023 za ta zama sauyi ga Najeriya, ina da kwarin gwiwa cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta kawo sauyi na ban mamaki ba a Najeriya kadai ba har ma da Afirka baki daya”.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp