Gwamantin Jihar Kano ta ce nan ba da jimawa ba za ta fara kama mabarata manya da yara da ke gararamba a fadin jihar.
Gwamantin ta bayyana haka ne ta bakin shugaban hukumar hana barace-barace, Sheikh Bakari Mika’il, ta na mai cewa dukkan yaran da aka kama hukuncinsu zai rataya ne kan iyayensa.
Sannan ta ce akwai tarar kuÉ—i kamar dai yadda dokar hana bara ta 2013 ta tanada. A cewar BBC.
Sai dai wasu daga cikin mazauna jihar na bayyana mabambamtan ra’ayi kan tasirin dokar.