Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya gargaɗi Hamas cewa za ta ɗanɗani kuɗarta kan abin da ya kira “zalunci da mugunta” da suka yi na saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta.
Kalaman nasa na zuwa ne bayan gwaje-gwajen binciken gawarwakin da Isra’ila ta yi ya nuna gawar da aka dawo da ita daga Gaza a ranar Alhamis ba ta ƴar Isra’ila Shiri Bibas da aka yi garkuwa da shi ba ne.
Hamas ta ce da alama an yi kuskuren sanya gawar Shiri Bibas cikin waɗanda aka binne cikin ɓaraguzai bayan wani harin Isra’ila ta sama a Gaza, wanda ta ce shi ne ya kasheta tare da ƴaƴanta biyu maza biyu ƙanana.
Gwajin ya tabbatar da gawarwakin yaran nata biyu da aka mayar ranar Alhamis.
Sai dai Isra’ila ta ce gwajin da aka yi ya nuna cewa ƴan ta’adda ne suka kashe su.
Tuni dai Hamas ta fitar da sunayen mutum shida masu rai da za a sako ranar Asabar