fidelitybank

Hamas ta tabbatar da sako Fursunoni 110 daga Isra’ila

Date:

Fursunoni 110, yawanci Falasɗinawa ne Isra’ila ta saka a cikin matakan tabbatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, inda ɓangarorin biyu suke musayar fursunonin yaƙi.

Daga cikin mutum 110 ɗin, 32 daga cikin an yanke musu hukuncin ɗaurin rai da rai ne, sannan akwai 48 da suke da ɗaurin zaman gidan yari masu tsawo.

Haka kuma a ciki akwai ƙananan yara, wanda ƙaramin ciki shi ne mai shekara 15.

Kafar yaɗa labaran Hamas ce ta tabbatar da sakin fursunonin guda 110, bayan Hamas ɗin ta saki Isra’ilawa uku, da ƴan ƙasar Thailand biyar da ke hannunta.

Wannan ce musayar fursunoni ta uku da aka yi tun bayan da aka shiga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanain Hamas da Isra’ila a ranar 19 ga Janairu. In ji BBC.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp