fidelitybank

Hamas ta saki ƙarin Isra’ilawa uku a Gaza

Date:

Bayan sanya hannu a dakardu tsakanin Hamas da wakiliyar ƙungiyar Red Cross, Hamas ta saki ƙarin mutum uku cikin waɗanda aka tsara za ta saki yau Asabar, ‘yan Isra’ila da ta yi garkuwa da su.

A wannan rukunin na mutum uku mayaƙan ƙungiyar sun fara sakin mutum na farko Eliya Cohen mai shekara 27.

Sai kuma suka saki Omer Shem Tov mai shekara 22 da kuma na uku Omer Wenkert, mai shekara 23, waɗanda Hamas ta kama su a bikin waƙe-waƙe na Nova, ranar 7 ga watan Oktoba na 2023, inda aka danƙa su ga ƙungiyar Red Cross a yau ɗin.

A wannan karon ana miƙa su ne a garin Nuseirat, wanda ke tsakiyar Zirin Gaza.

Bayahude na huɗu da aka tsara Hamas ɗin za ta saki yau shi ne Hisham al-Sayed, wanda ta yi garkuwa da shi tun 2015 bayan da ya tsallaka zuwa Gaza shi kaɗai.

Za kuma a sake shi ne nan gaba a yau ba tare da wani gangamin jama’a ba.

Ana sa ran Isra’ila za ta saki Falasɗainawa sama da 600 daga cikin waɗanda take tsare da su a gidajen yarinta a madadin Yahudawa huɗu da Hamas ke saki yau.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp