Hamas ta saki wasu ƴan Isra’ila biyu, Yarden Bibas mai shekara 34 da Ofer Kalderon mai shekara 53 a ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin biyu.
An miƙa mutanen ne ga ƙungiyar Red Cross a Khan Younis kuma tuni suka tsallaka kan iyaka daga Gaza zuwa cikin Isra’ila.
Ana sa ran Hamas ɗin za ta saki mutum na uku, Keith Seigel, kamar yadda ta alƙawarta zuwa anjima kadan.
An yi musayar waɗannan mutane uku ne da wasu Falasɗinawa sama da 180 da ake tsare da su a kurkukun Isra’ila.