Ƙungiyar Falasɗinawa ta Hamas ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawar zaman lafiya da Isra’ila ba har sai ta sako fursunoni Flasdinawa sama da 600 kamar yadda aka cim ma yarjejeniya tun da fari.
Isra’ila ta jinkirta sakin Falasdinawa sama da 600 a ranar Asabar bayan Hamas ta mika wa kungiyar agaji ta Red Cross Isra’ilawa shida masu rai da take garkuwa da su.
Firaminista Benjamin Netanyahu ya ce sun ɗauki matakin ne “har sai an tabbatar da sakin rukuni na gaba na mutanen da ake garkuwa da su, kuma sai Hamas ta daina gabatar da su a gaban ‘yankallo”.
Ya kuma yi barazanar a kowanne lokaci Isra’ila ka iya komawa yaƙin da suka kwashe sama da shekara suna gwabzawa a Zirin Gaza.
A farkon watan Maris ne wa’adin z farangoko na yarjejeniyar tsagaita wutar zai ƙare.