fidelitybank

Halin yau ne ya sa na sayar da Jika na ɗan wata uku – Nwosu

Date:

Wata mata mai suna Oluchukwu Nwosu ta sayar da jikanta mai watanni uku, inda ta bayyana cewa wahala da kasar ke ciki ne ya tura ta.

Matar wadda ‘yar asalin garin Nnewi ta jihar Anambra ce ta siyar da yaron akan kudi naira 50,000.

Matar a karshen mako ne jami’an ma’aikatar mata ta jihar Anambra suka kama matar, inda suka gabatar da ita gaban kwamishina, Ify Obinabo, inda ta amsa.

A cikin wani faifan bidiyo da jaridar DAILY POST ta gani, matar ta yi kuka sosai, inda ta ce an tura ta ne ta sayar da jaririn ne saboda ‘yarta ta kasance cikin halin daukar ciki, kuma ta bar ta da ‘ya’yan da za su kula da ita.

“Wannan shine karo na uku da ‘yata Ijeoma ke daukar ciki ba tare da aure ba. Saboda rashin kudin shigarmu mun fuskanci matsalar ciyarwa tun lokacin da diyata ta haifi jariri na farko.

“Ba mu da wani zabi da ya wuce mu kai yaran ga jarirai marasa uwa gida, musamman ma da ‘yarmu ta ki gaya mana wanda ke da alhakin daukar cikin ta.

“Na ci karo da wani mai saye mai suna Tochukwu Asiegbu, wanda ya tunkare ni, bayan an yi ciniki, ya biya ni kudaden da aka amince da su,” in ji ta.

Kwamishinan ya bayyana a faifan bidiyon cewa an ceto jaririn mai watanni uku.

“Mahaifiyar jaririn mai suna Ijeoma Nwosu ta zo wajenmu ta ce mahaifiyarta ta sayar da jaririn nata da karfi jim kadan bayan an haife shi kuma ta ki bayyana inda yake.

“Bayan samun wannan zarge-zargen, da sauri na zage damtse domin gano wadanda suka aikata laifin tare da damke su.

“Bayan wata guda da jami’an ma’aikatar tawa ta yi na ci gaba da sa ido kan bayanan sirri, an kama wadanda suka aikata laifin.

“Dukkan wadanda ke da hannu a cikin lamarin an kama su kuma an mika su ga ‘yan sanda domin bincike da gurfanar da su gaban kotu,” in ji kwamishinan.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp