Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayar da umarnin dakatar da wani basarake mai daraja ta daya, Ohi na Eganyi wanda ke rike da mukamin shugaban majalisar gargajiya ta Ajaokuta, Alhaji Musa Isah Achuja, ba tare da bata lokaci ba.
Gwamnan, a wata wasika da ya aikewa kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, ya umurci shugaban karamar hukumar Ajaokuta, Mustapha Aka’aba, da a tambayi shugaban karamar hukumar Ajaokuta, kan tabarbarewar tsaro a Ajaokuta tare da umartar shugaban da ya amsa cikin Sa’a 24.
Umarnin gwamnan ya biyo bayan tabarbarewar tsaro a yankin na baya-bayan nan wanda ya yi sanadin mutuwar wasu jami’an tsaro, bisa halalcinsu na tabbatar da doka da oda.
Gwamnan ya yi kakkausar gargadi ga sauran sarakunan gargajiya a fadin jihar da ka iya alakanta su ta wata hanya ko kuma wata alaka da masu aikata miyagun laifuka a yankunansu da su kau da kai.
A cewarsa, gwamnatinsa za ta yanke mu’amala da duk wanda ke soyayya da masu aikata laifuka komai girmansa.
Gwamna Yahaya Bello, a wata sanarwa a ranar, 31 ga watan Yuli, ta hannun babban sakataren yada labaran sa, Onogwu Muhammed, ya kuma umurci duk wani yunkuri na shugabannin kananan hukumomin na fita daga yankunansu da sauran tafiye-tafiye ba tare da bin ka’ida ba.
Gwamnan ya yi gargadin cewa, babu wata alaka da masu aikata miyagun laifuka da za su hana shi daga babban nauyin da ke kansa na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa da mazauna jihar.