fidelitybank

Halin Tsaro: Gwamna ya dakatar da Basarake mai daraja ta ɗaya a Kogi

Date:

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayar da umarnin dakatar da wani basarake mai daraja ta daya, Ohi na Eganyi wanda ke rike da mukamin shugaban majalisar gargajiya ta Ajaokuta, Alhaji Musa Isah Achuja, ba tare da bata lokaci ba.

Gwamnan, a wata wasika da ya aikewa kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, ya umurci shugaban karamar hukumar Ajaokuta, Mustapha Aka’aba, da a tambayi shugaban karamar hukumar Ajaokuta, kan tabarbarewar tsaro a Ajaokuta tare da umartar shugaban da ya amsa cikin Sa’a 24.

Umarnin gwamnan ya biyo bayan tabarbarewar tsaro a yankin na baya-bayan nan wanda ya yi sanadin mutuwar wasu jami’an tsaro, bisa halalcinsu na tabbatar da doka da oda.

Gwamnan ya yi kakkausar gargadi ga sauran sarakunan gargajiya a fadin jihar da ka iya alakanta su ta wata hanya ko kuma wata alaka da masu aikata miyagun laifuka a yankunansu da su kau da kai.

A cewarsa, gwamnatinsa za ta yanke mu’amala da duk wanda ke soyayya da masu aikata laifuka komai girmansa.

Gwamna Yahaya Bello, a wata sanarwa a ranar, 31 ga watan Yuli, ta hannun babban sakataren yada labaran sa, Onogwu Muhammed, ya kuma umurci duk wani yunkuri na shugabannin kananan hukumomin na fita daga yankunansu da sauran tafiye-tafiye ba tare da bin ka’ida ba.

Gwamnan ya yi gargadin cewa, babu wata alaka da masu aikata miyagun laifuka da za su hana shi daga babban nauyin da ke kansa na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa da mazauna jihar.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp