Tsohon shugaban ƙasa, Ibrahim Badamasi Babagida IBB, ya nuna matuƙar damuwa dangane da halin da kasar ta tsinci kanta na taɓarɓarewar tsaro.
A wata hira da ya yi da BBC, Ibrahim Babangida, ya ce, yanzu akwai bukatar ‘yan kasar su dage da addu’o’in samun sassauci daga kashe-kashen da suka yawaita a sassan kasar.
Sannan ya jaddada bukatar bai wa jami’an tsaro hadin-kai don kakkaɓe ɓata-gari.
Tsohon shugaban ƙasar na mulkin soja, ya ce ya wajaba a janyo hankali a’lummar kasar da su nuna jajircewa da yin addu’oi da kyakkyawan fata ga Najeriya saboda ‘yan kasar ba su da wata kasa bayan ita.
“Tilas mu tabbabatar mun yi wa kasarmu addu’a, domin neman hadin-kan kasa da al’umma baki daya,” in ji shi.