Hare-haren ‘yan bindiga ya tilastawa hakimai a yankin Bashar da ke karamar hukumar Wase ta jihar Filato barin gari ba shiri.
An tattaro cewa masu garkuwa da mutane na ta kaddamar da hare-hare tare da karbe ragamar iko a wasu garuruwa a yankin Wase.
Wani mazaunin yankin ya ce, yan bindigar kan sace mutane tare da neman kudin fansa, sannan cewa su kan kashe wanda bai da kudin biya ko su daddaure shi.
A cewar Daily Trust, ta ce, garin Bashar ya kasance mahaifar mataimakin kakakin majalisar wakilai, Idris Ahmed Wase.