fidelitybank

Hakar Ma’adanai: An tsamo gawarwaki a kalla mutane 32 a Sudan

Date:

Masu aikin ceto na ci gaba da kokarin curo wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata daga wata mahakar zinare a wani yanki mai nisa a kasar Sudan.

Lamarin ya faru ne tun a ranar lahadi, inda akalla mutane 32 su ka mutu a cikin ramin da ya rufta dasu.

Ya zuwa safiyar Larabar, an gano gawarwaki 32 daga mahakar ma’adinan a yammacin Kordofan baya ga wasu mutane uku da aka ceto sun jikkata, kamar yadda, Khaled Dahweya, daraktan kamfanin albarkatun ma’adinai na Sudan mallakin gwamnatin jihar a yammacin Darfur ya sanar da hakan a ranar Laraba.

Mahakar ma’adinan ta rufta ne da yammacin Lahadin da ta gabata, yayin da, kimanin mutane 40 ne ake kyautata zaton na cikin ramin mai zurfin sama da mita 20 (kafa 65).

Ya kara da cewa, hatsarin ya afku ne a yankin da ake yawan hako ma’adinai ba tare da la’akari da ka’idojin tsaro ba.

Zinariya ita ce kayayyaki mafi daraja a kasar Sudan wanda ake kai su zuwa ketare, amma yawancin karafan ana siyar da su a wajen tashoshi na hukuma, galibi ana siyarwa a Dubai.

Kasar Sudan dai ta sha fama da matsalar tattalin arziki da ta dade tana fama da shi, wasu kuma sun koma aikin hako ma’adinai a yankunan da ba su ci gaba ba, domin kokarin samun rayuwa.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp