fidelitybank

Hakar Ma’adanai: An tsamo gawarwaki a kalla mutane 32 a Sudan

Date:

Masu aikin ceto na ci gaba da kokarin curo wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata daga wata mahakar zinare a wani yanki mai nisa a kasar Sudan.

Lamarin ya faru ne tun a ranar lahadi, inda akalla mutane 32 su ka mutu a cikin ramin da ya rufta dasu.

Ya zuwa safiyar Larabar, an gano gawarwaki 32 daga mahakar ma’adinan a yammacin Kordofan baya ga wasu mutane uku da aka ceto sun jikkata, kamar yadda, Khaled Dahweya, daraktan kamfanin albarkatun ma’adinai na Sudan mallakin gwamnatin jihar a yammacin Darfur ya sanar da hakan a ranar Laraba.

Mahakar ma’adinan ta rufta ne da yammacin Lahadin da ta gabata, yayin da, kimanin mutane 40 ne ake kyautata zaton na cikin ramin mai zurfin sama da mita 20 (kafa 65).

Ya kara da cewa, hatsarin ya afku ne a yankin da ake yawan hako ma’adinai ba tare da la’akari da ka’idojin tsaro ba.

Zinariya ita ce kayayyaki mafi daraja a kasar Sudan wanda ake kai su zuwa ketare, amma yawancin karafan ana siyar da su a wajen tashoshi na hukuma, galibi ana siyarwa a Dubai.

Kasar Sudan dai ta sha fama da matsalar tattalin arziki da ta dade tana fama da shi, wasu kuma sun koma aikin hako ma’adinai a yankunan da ba su ci gaba ba, domin kokarin samun rayuwa.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp