Masu aikin ceto na ci gaba da kokarin curo wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata daga wata mahakar zinare a wani yanki mai nisa a kasar Sudan.
Lamarin ya faru ne tun a ranar lahadi, inda akalla mutane 32 su ka mutu a cikin ramin da ya rufta dasu.
Ya zuwa safiyar Larabar, an gano gawarwaki 32 daga mahakar ma’adinan a yammacin Kordofan baya ga wasu mutane uku da aka ceto sun jikkata, kamar yadda, Khaled Dahweya, daraktan kamfanin albarkatun ma’adinai na Sudan mallakin gwamnatin jihar a yammacin Darfur ya sanar da hakan a ranar Laraba.
Mahakar ma’adinan ta rufta ne da yammacin Lahadin da ta gabata, yayin da, kimanin mutane 40 ne ake kyautata zaton na cikin ramin mai zurfin sama da mita 20 (kafa 65).
Ya kara da cewa, hatsarin ya afku ne a yankin da ake yawan hako ma’adinai ba tare da la’akari da ka’idojin tsaro ba.
Zinariya ita ce kayayyaki mafi daraja a kasar Sudan wanda ake kai su zuwa ketare, amma yawancin karafan ana siyar da su a wajen tashoshi na hukuma, galibi ana siyarwa a Dubai.
Kasar Sudan dai ta sha fama da matsalar tattalin arziki da ta dade tana fama da shi, wasu kuma sun koma aikin hako ma’adinai a yankunan da ba su ci gaba ba, domin kokarin samun rayuwa.