fidelitybank

Hakar Ma’adanai: An tsamo gawarwaki a kalla mutane 32 a Sudan

Date:

Masu aikin ceto na ci gaba da kokarin curo wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata daga wata mahakar zinare a wani yanki mai nisa a kasar Sudan.

Lamarin ya faru ne tun a ranar lahadi, inda akalla mutane 32 su ka mutu a cikin ramin da ya rufta dasu.

Ya zuwa safiyar Larabar, an gano gawarwaki 32 daga mahakar ma’adinan a yammacin Kordofan baya ga wasu mutane uku da aka ceto sun jikkata, kamar yadda, Khaled Dahweya, daraktan kamfanin albarkatun ma’adinai na Sudan mallakin gwamnatin jihar a yammacin Darfur ya sanar da hakan a ranar Laraba.

Mahakar ma’adinan ta rufta ne da yammacin Lahadin da ta gabata, yayin da, kimanin mutane 40 ne ake kyautata zaton na cikin ramin mai zurfin sama da mita 20 (kafa 65).

Ya kara da cewa, hatsarin ya afku ne a yankin da ake yawan hako ma’adinai ba tare da la’akari da ka’idojin tsaro ba.

Zinariya ita ce kayayyaki mafi daraja a kasar Sudan wanda ake kai su zuwa ketare, amma yawancin karafan ana siyar da su a wajen tashoshi na hukuma, galibi ana siyarwa a Dubai.

Kasar Sudan dai ta sha fama da matsalar tattalin arziki da ta dade tana fama da shi, wasu kuma sun koma aikin hako ma’adinai a yankunan da ba su ci gaba ba, domin kokarin samun rayuwa.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp