fidelitybank

Haka kurin laifin wani ya shafe ni ban amince ba – Shugaban EFCC

Date:

Shugaban hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati EFCC, AbdulRasheed Bawa ya ce, ya daukaka kara dangane da hukuncin da wata kotun birnin tarayya ta yanke masa ranar Talata a Abuja.

Kotun yanke hukuncin tura shi gidan yari sakamakon kama shi da laifin raina umarnin kotu.

Tun da farko dai kotun ta umarci shugaban da ya mayar da wasu kudi da suka kai naira miliyan 40 da wata motar alfama da hukumar ta karba daga wani mutum da ta zarga da laifin rashawa.

Shugaban EFCC, ya ce, shi a karan kansa bai yi watsi da umarnin kotun ba a matsayinsa na shugaban hukumar, ballantana ya fuskanci fushin kotu, saboda a saninsa kotun ta bayar da umarnin ne tun a ranar 21 ga watan Nuwamban 2018.

Wato shekara uku kenan kafin ya zama shugaban hukumar ta EFCC, dan haka ba shi aka bai wa umarnin ba kuma a cewarsa babu yadda za a yi laifin wani ya shafe,

Ya kara da cewa ”Mun riga mun daukaka kara game da wannan hukunci, dan haka za mu jira domin ganin yadda shari’ar za ta kasance”

Amma ya ce duk da haka ya bayar da umarni a mayar da wannan motar alfarma ga mai ita tun a ranar 27 ga watan Yunin wannan shekarar, tare da bayar da umarnin bin hanyar da ta dace wajen mayar da kudin naira miliyan 40 ga mai su.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp