Babban mataimaki na musamman kan harkokin zabe ga gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi, wato Mista Olaiya Kupolati, ya yi murabus daga APC ya koma jamâiyyar Social Democratic Party (SDP).
Kupolati ya ce, murabus din nasa ya fara aiki ne a ranar 30 ga Maris, 2022, a wata wasika mai dauke da kwanan wata 23 ga Maris, 2022, da kuma aikewa ofishin sakataren gwamnatin jihar.
Kupolati ya bayyana cewa, murabus din nasa ya biyo bayan sabuwar dokar zabe ne, wanda ya bukaci duk wani wanda aka nada da ke neman mukamin siyasa ya yi murabus kamar yadda doka ta tanada, kuma yana da niyyar tsayawa takarar majalisar wakilai a kan jam’iyyar SDP.
Tsohon hadimin Fayemi ya ci gaba da cewa, yin aiki da bainar jamaâarsa a zaben gwamnan da za a yi ranar 18 ga watan Yuni zai zama babban cin amana. Kupolati ya kuma bayyana a hukumance cewa ya tsaya takarar dan majalisar wakilai mai wakiltar jihar Ilejemeje a zaben 2023.