Tsohon hadimin shugaba Muhammadu Buhari, kan kafafen sada zumunta Bashir Ahmed da ke nema takarar dan majalisar wakilai ya yi watsi da sakamakon zaben fidda gwani da aka yi a Kano.
Bashir Ahmed wanda ke neman wakiltar kananan hukumomin Gaya da Ajingi da Albasu ne a matsayin tarayya, ya kafa hujjar rikici a matsayin dalilin da ya sanya ya yi watsi da sakamakon.
Rahotanni sun bayyana cewa an kasa cimma maslaha tsakanin ‘yan takara da dama a mazabu masu yawa.
Ciki kuwa har da Fagge da Kano Municipal da Baya da Ajingi da Albasu, Kiru da Bebeji da dai sauransu.
Ya yi zargin kawo ‘yan daba domin tayar da hankali da ganin ba a yi zaben ba yadda ya kamata, ya ce hakan yasa ya fice daga dakin zaben saboda tsaro.
An bayyana dan majalisar tarayya da ke ci a yanzu Abdullahi Mahmood Gaya a matsayin wanda ya lashe zaben.