Tsohon gwamnan jihar Kano, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Rabi’u Kwankwanso, ya bayyana dalilin da ya sa ba za a iya dorewar kawancen jam’iyyarsa da jam’iyyar Labour (LP) ba.
Kwankwanso, wanda ya yi jawabi ga ‘ya’yan jam’iyyar a Gombe ranar Asabar, ya yi nuni da cewa, ba zai iya amincewa da zama abokin takarar kowa ba, saboda ci gaban jam’iyyarsa.
An gudanar da shawarwari tsakanin NNPP da LP domin kulla kawance gabanin babban zaben 2023.
Bisa ga gaggarumin gazawar da gwamnatin APC ta yi a yanzu, ‘yan Najeriya da dama sun yi tir da tikitin takarar Obi-Kwankwanso a matsayin hanyar rusa manyan jam’iyyun kasar nan.
Da yake magana kan wannan ci gaban, Kwankwanso ya bayyana cewa, zabi daya da ake da shi shine Peter Obi ya zama abokin takararsa.
Ya jaddada cewa, hakan zai kara wa yankin Kudu-maso-Gabas fatan zama shugaban kasa a shekaru masu zuwa.
Ya ce: “Daga tattaunawar da aka yi da jam’iyyar Labour, babban batu shi ne wanda zai zama shugaban kasa idan jam’iyyun suka hade.