Hukumar kiyaye haɗura ta jihar Kogi, ta tabbatar da mutuwar mutum shida yayin da wasu 25 suka samu raunuka a haɗarin mota kan hanyar Okene-Ogori da ke jihar Kogi yau Asabar.
Babban kwamandan hukumar, mista Stephen Dawulung, ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN a Lokoja cewa haɗarin ya faru ne lokacin da wata mota dauke da mutane 45 da kuma wasu shanu.
Kwamandan ya ce haɗarin wanda ya faru da misalin 12 na rana, ya yi sanadiyar mutuwar wasu daga cikin shanun.
Ya kara da cewa bayan faruwar lamarin, ya aike da jami’ansa zuwa wurin, inda a halinn aka tafi da wadanda suka samu raunuka zuwa asibiti domin yi musu magani yayin da aka girke gawarwakin wadanda suka rasu a mutuware da ke garin na Okene.
Babban kwamandan ya yi kira ga direbobi da su kasance masu bin dokokin hanya a kodayaushe domin afkuwar haɗari da tsira da rayukansu.