fidelitybank

Gwanar da ta shafe kwanaki 10 ta na girki ba kakkautawa

Date:

Gwanar girkin ƙasar Ghana Failatu Abdul-Razak ga alama ta karya tarihin duniya, bayan ta kwashe tsawon fiye da sa’a 227 tana zuba girki babu ƙaƙƙautawa.

Lulluɓe da tutar ƙasar, Failatu Abdul-Razak ta kawo ƙarshen girkin tsawon kwana goma, cikin jinjina da yabo daga cincirindon mutane a ranar Laraba.

Gabanin ta fara girkin nata, ta bayyana fafutukar da ta sanya gaba a matsayin “aikin ƙasa”, inda ta ce tana yi ne domin Ghana.

Mutane sun yi ta sowa lokacin da ta fito daga ɗakin girke-girke na otel ɗin da ta yi bajintar a birnin Tamale.

Jami’an da ta yi aiki da su, sun ce za ta aika shaidar aikinta ga kundin bajinta na duniya Guinness World Records don tabbatarwa bisa ƙa’ida cewa ta karya tarihin da aka taɓa kafawa a baya.

Mai riƙe da kambin tarihin na yanzu ɗan ƙasar Ireland Alan Fisher, ya yi girki tsawon sa’a 113 da minti 57.

Gwanar girkin ta Ghana ta ce tana so ne ta tabbatar cewa duk wanda ya yi ƙoƙarin karya tarihinta, sai ya sha matuƙar “wahala”.

‘Yan siyasa, ciki har da mataimakin shugaban ƙasa Mahamudu Bawumia, da ɗumbin fitattun mutane kai har da rundunar sojojin Ghana sun bayyana goyon bayansu ga gwanar girkin a tsawon lokacin da ta ɗora sanwa.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp