Gwamnonin jihohin Zamfara da Katsina Dauda Lawal da Dikko Radda sun yi wata ganawar sirri da ministan tsaro, Badaru Abubakar da kuma mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu a Abuja.
Ganawar da aka yi tun jiya Talata, bayanai na nuna cewa ta mayar da hankali ne kan samar da hanyoyin da za su haɗa ƙarfi da ƙarfe tar da duba sabbin hanyoyin da za a bi domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankunansu.
A wata sanarwa da mai magana da yawun Zamfara Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce gwamnonin sun tattauna wa ministan da mai ba shugaban ƙasar shawara ne a kan wasu shawarwari da haɗakar ƙungiyoyin arewa wato CNG suka gabatar domin samar da zaman lafiya a jihohinsu, da sauran abubuwan da suka shafi tsaro.
Taron ya kuma samu halartar shugaban kwamitin amintattu na NCG, Alhaji Nastura Ashir Shariff da sauran mambobin kwamitin tsaro na ƙungiyar.