fidelitybank

Gwamnonin Zamfara da Benue sun ƙalubalanci gayyatar kwamitin majalisar wakilai

Date:

Gwamnonin jihohin Zamfara da Benue, Dauda Lawal da Hyacinth Alia, sun ƙi amincewa da gayyatar da Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafe na Majalisar Wakilai ta Tarayya ya aike musu, inda suka bayyana shakku kan halaccin gayyatar.

An gayyaci gwamnonin da majalisun dokokin jihohinsu ne domin su bayyana a gaban kwamitin bisa zargin karya ƙundin tsarin mulki da kuma gazawa wajen gudanar da mulki.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na kwamitin, Chooks Oko, ya fitar

Sanarwar ta bayyana cewa an tsara zaman sauraron bayanansu ne a ranar 8 ga watan Maris, inda ake sa ran za su bayar da ƙarin haske kan wasu muhimman al’amura.

Daga cikin matsalolin da ake son jin bayani a kansu har da dakatar da wasu ‘yan majalisar jiha da kuma taɓarɓarewar tsaro a jihohin biyu.

Hakan ya sa majalisar ke duba yiwuwar amfani da Sashe na 11(4) na Ƙundin Tsarin Mulki na 1999, domin ɗaukar ragamar ayyukan majalisun dokokin jihohin idan an ga hakan ya zama dole.

A Jihar Benue, an dakatar da ‘yan majalisa 13 bayan da suka nuna adawa da cire shugaban alƙalan jihar, Mai shari’a Maurice Ikpambese, wanda gwamnan ya jagoranta.

An dauki dakatarwar dai a matsayin ramuwar gayya ga ‘yan majalisar da ba sa goyon bayan gwamnan.

A Jihar Zamfara kuwa, lamarin shine wasu ‘yan majalisa tara da aka dakatar suka kafa wani rukunin majalisa daban, suna kuma ci gaba da iƙirarin cewa suna da cikakken ikon dokoki.

Yanzu haka, majalisar wakilai ta tarayya na ci gaba da nazarin ko lamarin ya kai matakin da ya dace a shiga tsakani ta hanyar karɓar ragamar aikin majalisun jihohin.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp