fidelitybank

Gwamnonin PDP sun janye dakatarwar da suka yi wa shugaban jam’iyya na ƙasa

Date:

Gwamnonin babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP sun soke dakatarwar da aka yi wa muƙaddashin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Iliya Damagum.

Gwamnonin sun kuma soke dakatarwar da aka yi wa sakataren hulɗa na ƙasa na jam’iyyar, Debo Ologunagba, da mai ba da shawara kan harkokin shari’a, Kamaldeen Ajibade.

Wannan na kunshe ne cikin jawabin da shugaban gwamnonin jam’iyyar kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya yi wa manema labarai a safiyar yau Talata.

Bala ya ce Damagum ne shugaban jam’iyyar da suka sani yanzu kuma shi zai ci gaba da riƙe kujerar.

Tun da farko dai, wani ɓangaren kwamitin zartaswar jam’iyyar na ƙasa da ya ɓalle ya sanar da naɗa Yayari Mohammed a matsayin wanda zai maye gurbin Damagum, inda kowane ɓangare ya yi iƙirarin dakatar da ɗayan.

A wata sanarwa ranar Lahadi, Yayari ya ce kwamitin zartaswar jam’iyyar ya naɗa shi ne domin mayar da dawo da jam’iyyar kan turba.

Ya ce PDP ba ta yin adawa yadda ya kamata saboda kowa ya ɗora buƙatar kansa a gaba kafin ta jam’iyya – musamman ma wasu jagororin kwamitin na zartaswa.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp