Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama kuma dan jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Majalisar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa, Femi Fani Kayode ya yi ikirarin cewa, gwamnoni shida na jam’iyyar PDP, za su bayyana goyon bayansu ga Tinubu a watan Janairun 2023.
Kayode ya bayyana hakan ne a shafin sa na Twitter ranar Juma’a.
Ya kara da cewa za a yi watsi da ikirarin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Abubakar Atiku na lashe zaben 2023.
“Sanarwar goyon bayan da @officialABAT za ta samu daga gwamnoni 6 (ba wai guda 5) daga @OfficialPDPNig a wannan watan Janairu zai kawo karshen rugujewar da @atiku ya yi taurin kai game da lashe zaben shugaban kasa a 2023. Idanunsa za su fita da wuri”, in ji shi.