fidelitybank

Gwamnonin Kudu sun yabawa Badaru bisa janyewa da ya yi

Date:

Ƙungiyar gwamnonin kudancin Najeriya ta Southern Governors Forum (SGF) ta yaba wa takwarorinsu na arewaci musamman Badaru Abubakar na Jihar Jigawa game da janyewa daga neman takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC da ya yi.

Wata sanarwa da shugaban SGF kuma Gwamnan Jihar Ondo Rotimi Akeredolu ya sanya wa hannu ta ce “da ma abin da muke tsammani ke nan daga ‘yan uwanmu masu kishin ƙasa”.

Sanarwar ta nemi sauran ‘yan takara daga Arewa da su yi koyi da Gwamna Badaru wajen janyewa su ƙyale ‘yan Kudu su fafata a akwatin zaɓe.

“Muna taya ɗan uwanmu Gwamna Badaru murna game da halin kirki da ya nuna,” a cewar sanarwar. “Har abada za a dinga yaba masa.”

Sai dai Badaru ya faɗa wa BBC Hausa cewa yana jiran Shugaba Buhari ya amince da janyewar tasa tukunna.

Bayan ganawarsu da shugaban ƙasa, su ma gwamnonin kudancin Najeriya ƙarƙashin jagorancin Akeredolu suka yi wata ganawa a Abuja babban birnin ƙasar ranar Asabar da dare.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...
X whatsapp