Da alamu dai rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya zo karshe bayan da shugabannin jam’iyyar suka cimma matsaya da gwamnonin PDP na G5.
Mambobin Gwamnonin PDP G5, karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, sun yi takun-saka da Atiku, bayan da Wike ya kasa lashe tikitin takarar shugaban kasa na jamâiyyar.
Sauran mambobin G5 sun hada da: Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo, Samuel Ortom na jihar Benue, Okezie Ikpeazu na jihar Abia, da Ifeanyi Ugwuanyi na jihar Enugu.
Haka kuma G5 din ba su ji dadin yadda Atiku ya ki amincewa da Wike a matsayin mataimakinsa ba tare da neman Iyorchia Ayu ya sauka daga mukaminsa na Shugaban jamâiyyar, bisa zarginsa da rage karfin jamâiyyar PDP daga Arewa.
Sai dai kuma alamu sun nuna cewa da alama tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (rtd) ne ya kawo karshen rikicin da ya dabaibaye babbar jamâiyyar adawa.
Wani jigon jamâiyyar, wanda ya gwammace a sakaya sunansa, ya ce, G5 sun amince su yi wa dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar, Atiku Abubakar aiki, idan har za a biya musu sabbin bukatunsu.
Bukatun nasu, a cewar majiya mai tushe, ita ce: âYa kamata a raba manyan maâaikatun gwamnati tsakanin shiyyoyin siyasa guda shida;
“Ya kamata a raba manyan jami’an tsaro a dukkan shiyyar siyasa da kuma cewa dukkan ofisoshin jam’iyyar a Kudu su koma Arewa idan Atiku ya yi nasara.”