Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya ce, jam’iyyar PDP na da hanyoyin da za ta bi wajen hukunta mambobin da suka yi kuskur suka marawa wata jam’iyyar baya.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa dauke da sa hannun mai baiwa Tambuwal shawara kan harkokin yada labarai, Muhammad Bello, ranar Juma’a.
Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta cece-kuce kan gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike wanda ya fi son takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Tambuwal ya aike da gargadi ga Wike da wasu gwamnonin da ake zargin suna shirin yin aiki sabanin muradun jam’iyyar.
Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Jam’iyyar PDP za ta mayar da martani game da bata-gari na wasu gwamnoninta biyar da ake rade-radin cewa suna dambarwar siyasa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Ahmed Tinubu.
Tambuwal ya aike da gargadi ga Wike da wasu gwamnonin da ake zargin suna shirin yin aiki sabanin muradun jam’iyyar.
Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Jam’iyyar PDP za ta mayar da martani game da bata-gari na wasu gwamnoninta biyar da ake rade-radin cewa suna dambarwar siyasa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Ahmed Tinubu.
“PDP jam’iyya ce mai bin doka da oda, kuma za ta binciki hanyoyin da suka dace don kawo duk wani mambobinta da suka yi kuskure.”
Ya kara da cewa idan Wike da sauran gwamnonin da ke tare da shi suka yanke shawarar abin da za su yi, jam’iyyar za ta mayar da martani ga duk wani matsayi da suka dauka.