Dan takarar gwamnan PDP a jihar Ogun, Hon. Ladi Adebutu, ya bukaci gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike da sauran wadanda suka kasa amincewa da Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar PDP na kasa da su fice daga jam’iyyar.
Wike da wasu gwamnoni hudu na jam’iyyar PDP sun dage cewa Ayu ya yi murabus a matsayin shugaban jam’iyyar ko kuma ba za su goyi bayan takarar shugaban kasa na Atiku Abubakar ba.
A cewarsu, Ayu ya yi alkawarin cewa zai yi murabus idan dan arewa ya fito a matsayin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.
Bayan da Atiku ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da aka gudanar a watan Mayu, Wike da magoya bayansa sun sha rokon Ayu da ya yi murabus, duk da kokarin kwantar da hankulan su ya ci tura.
Ya kara da cewa: “Mu maida hankali, nan da ‘yan makonni masu zuwa za mu samu ‘yanci; kuma idan mun sami ‘yanci za mu ci gaba da tafiya”.
Ya zargi jam’iyyar APC mai mulki da gazawa wajen samar da tsaro, kyakkyawan shugabanci da abinci ga talakawa.