Gwamnonin jihohi da aka zaba a karkashin jam’iyya mai mulkin kasar ta APC, sun ki amicewa da wa’adin 10 ga watan Fabrairu da babban bankin Najeriya ya shata wa al’ummar kasar na su kamala sauya tsofaffin takardun naira na N1000, N500 and N200 da sababbin da ya fitar.
Gwamnonin sun ce bayanan da ke isa garesu daga al’umominsu sun tabbatar musu cewa al’umomin na shan bakar wahala cikin ‘yan kwanakin da suka gabata yayin da suke kokarin sauya takardun kudin, saboda lokacin da bankin ya bayar bai zo a lokacin da ya dace ba da kuma dalilin illar da matakin ke yi wa tattalin arzikin kasar.
Wannan ne yasa suka yanke shawarar ganawa da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da misalin karfe 10 na safiyar Juma’a.
Karanta Wannan:Â Da Dumi Dumi: CBN ya umarci Bankuna su fara biyan sababbin kudi
Cikin jihohi 36 na Najeriya, jam’iyyar APC na iko da jihohi 21 ne.
Gabanin yanke wannan hukuncin ganawa, gwamnonin sun zabi gwamna Babajide Sanwo-Olu (Lagos) da Nasir El-Rufai (Kaduna) da Mai Mala Buni (Yobe) da kuma Dapo Abiodun (Ogun) domin su gana da gwamnan babban bankin Godwin Emefiele, kuma yayin tattaunawar da suka yi, sun sanar da shi rashin gamsuwarsu da “garaje da hanzarin” da ake nunawa na aiwatar da sauyin takardun kudin.
Sun kuma sanar da Mista Emefiele cewa babban bankin Najeriya ya gaza a aikin da aka ba shi na sauya takardun kudin ganin yadda ‘yan Najeriya ke fafutukar karbar takardun kudinsu da suka ajiye da kawunansu a bankunan kasar.