fidelitybank

Gwamnonin APC sun ki amincewa da wa’adin CBN

Date:

Gwamnonin jihohi da aka zaba a karkashin jam’iyya mai mulkin kasar ta APC, sun ki amicewa da wa’adin 10 ga watan Fabrairu da babban bankin Najeriya ya shata wa al’ummar kasar na su kamala sauya tsofaffin takardun naira na N1000, N500 and N200 da sababbin da ya fitar.

Gwamnonin sun ce bayanan da ke isa garesu daga al’umominsu sun tabbatar musu cewa al’umomin na shan bakar wahala cikin ‘yan kwanakin da suka gabata yayin da suke kokarin sauya takardun kudin, saboda lokacin da bankin ya bayar bai zo a lokacin da ya dace ba da kuma dalilin illar da matakin ke yi wa tattalin arzikin kasar.

Wannan ne yasa suka yanke shawarar ganawa da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da misalin karfe 10 na safiyar Juma’a.

Karanta Wannan: Da Dumi Dumi: CBN ya umarci Bankuna su fara biyan sababbin kudi

Cikin jihohi 36 na Najeriya, jam’iyyar APC na iko da jihohi 21 ne.

Gabanin yanke wannan hukuncin ganawa, gwamnonin sun zabi gwamna Babajide Sanwo-Olu (Lagos) da Nasir El-Rufai (Kaduna) da Mai Mala Buni (Yobe) da kuma Dapo Abiodun (Ogun) domin su gana da gwamnan babban bankin Godwin Emefiele, kuma yayin tattaunawar da suka yi, sun sanar da shi rashin gamsuwarsu da “garaje da hanzarin” da ake nunawa na aiwatar da sauyin takardun kudin.

Sun kuma sanar da Mista Emefiele cewa babban bankin Najeriya ya gaza a aikin da aka ba shi na sauya takardun kudin ganin yadda ‘yan Najeriya ke fafutukar karbar takardun kudinsu da suka ajiye da kawunansu a bankunan kasar.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp