Shugaban kungiyar gwamnonin Progressive Forum kuma gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, ya yi watsi da ikirarin cewa, wasu gwamnonin jam’iyyar, APC, na tattaunawa da jam’iyyar, PDP, da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar.
Bagudu ya ce gwamnonin APC ba sa aiki tare da PDP a kan burin dan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki, Bola Tinubu.
Ya bayyana hakan ne a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Kano a jiya.
Bagudu ya ba da tabbacin cewa gwamnonin APC na bayan burin Tinubu na shugaban kasa.
A cewar Bagudu: “Dukkan gwamnoninmu suna goyon bayan takarar Tinubu.
“Ikirarin da wasu ke yi na cewa wasu gwamnonin APC na tattaunawa da ‘yan adawa karya ne. Dukkan gwamnoninmu suna goyon bayan takarar Tinubu.”
Musanya tasa ta zo ne lokacin da Gwamna Nyesom Wike ya yi zargin cewa wasu gwamnonin APC na aiki da Atiku.